Watchtower LABURARE NA INTANE
Watchtower
LABURARE NA INTANE
Hausa
Ɓ
  • Ā
  • ā
  • Ɓ
  • ɓ
  • ɗ
  • Ɗ
  • Ƙ
  • ƙ
  • ꞌY
  • ꞌy
  • LITTAFI MAI TSARKI
  • WALLAFE-WALLAFE
  • TARO
  • lfb darasi na 84 p. 196-p. 197 par. 4
  • Yesu Ya Yi Tafiya a Kan Teku

Babu bidiyo don wannan zabin

Yi hakuri, bidiyon na da dan matsala

  • Yesu Ya Yi Tafiya a Kan Teku
  • Darussa daga Littafi Mai Tsarki
  • Makamantan Littattafai
  • Yesu Zai Iya Kāre Mu
    Ka Koya Daga Wurin Babban Malami
  • Jirgi Ya Yi Haɗari A Tsibiri
    Littafina na Labarun Littafi Mai Tsarki
  • Ya Shawo Kan Tsoro da Kuma Shakka
    Ka Yi Koyi Da Bangaskiyarsu
  • Ya Yaƙi Tsoro da Kuma Shakka
    Hasumiyar Tsaro Mai Shelar Mulkin Jehobah—2010
Dubi Ƙari
Darussa daga Littafi Mai Tsarki
lfb darasi na 84 p. 196-p. 197 par. 4
Yesu ya ce wa Bitrus ya zo wurinsa sa’ad da yake tafiya a kan ruwa

DARASI NA 84

Yesu Ya Yi Tafiya a Kan Teku

Ba ƙarfin warkar da marasa lafiya da kuma ta da matattu kawai Yesu yake da shi ba, amma yana da iko a kan iska da ruwa. Bayan Yesu ya yi addu’a a kan dutse, sai ya ga ana iska mai ƙarfi a Tekun Galili. Manzanninsa suna cikin jirgin suna fama. Sai Yesu ya sauko daga tudun kuma ya soma tafiya a kan ruwan tekun. Ya nufi wurin manzanninsa. Sa’ad da suka ga mutum yana tafiya a kan ruwa, sai suka ji tsoro. Amma Yesu ya ce musu: ‘Ni ne. Kada ku ji tsoro.’

Yesu ya ce wa Bitrus ya zo wurinsa sa’ad da yake tafiya a kan ruwa

Sai Bitrus ya ce: ‘Ubangiji, idan kai ne da gaske, ka ce in zo wurinka.’ Yesu ya ce wa Bitrus: ‘Ka zo.’ Sai Bitrus ya sauko daga jirgin, ya soma zuwa wurin Yesu. Amma sa’ad da ya kusa da Yesu, sai ya kalli iskar kuma ya ji tsoro, ya soma nitsewa. Bitrus ya yi ihu, ya ce: ‘Ubangiji, ka cece ni!’ Yesu ya riƙe hannunsa, ya ce: ‘Me ya sa ka soma shakka? Ina bangaskiyarka take?’

Sai Yesu da Bitrus suka shiga jirgin, kuma nan da nan iskar ta tsaya. Ka yi tunanin yadda manzannin suka ji? Sun ce: “Hakika, kai Ɗan Allah ne.”

Ba a wannan lokaci ne kaɗai Yesu ya nuna iko a kan iska ba. Amma akwai lokacin da manzanninsa suke tsallake teku, sai Yesu ya soma barci a cikin jirgin. Sa’ad da yake barci, sai aka soma iska mai ƙarfi. Iskar ta soma nitsar da jirgin. Manzannin suka ta da Yesu daga barci, da ihu suna cewa: ‘Malam, za mu mutu! Ka taimake mu!’ Sai Yesu ya farka daga barci kuma ya ce wa tekun: “Ka natsu!” Nan da nan iskar ta tsaya kuma tekun ya natsu. Yesu ya tambayi manzanninsa cewa: ‘Ina bangaskiyarku take?’ Sai suka ce wa juna: “Har iska da teku suna biyayya da shi.” Manzannin sun koya cewa ba sa bukatar su ji tsoro idan sun dogara ga Yesu.

“Da ina ne zan kasance, da ban gaskata cewa zan ga alherin Jehobah a cikin ƙasa ta masu rai ba?”​—Zabura 27:​13, New World Translation

Tambayoyi: Me ya sa Bitrus ya soma nitsewa? Wane darasi ne manzannin Yesu suka koya daga wurinsa?

Matta 8:​23-27; 14:​23-34; Markus 4:​35-41; 6:​45-52; Luka 8:​22-25; Yohanna 6:​16-21

    Littattafan Hausa (1987-2026)
    Fita
    Shiga Ciki
    • Hausa
    • Raba
    • Wadda ka fi so
    • Copyright © 2026 Watch Tower Bible and Tract Society of Pennsylvania
    • Ka'idojin Amfani
    • Tsarin Tsare Sirri
    • Saitin Tsare Sirri
    • JW.ORG
    • Shiga Ciki
    Raba