Watchtower LABURARE NA INTANE
Watchtower
LABURARE NA INTANE
Hausa
Ɓ
  • Ā
  • ā
  • Ɓ
  • ɓ
  • ɗ
  • Ɗ
  • Ƙ
  • ƙ
  • ꞌY
  • ꞌy
  • LITTAFI MAI TSARKI
  • WALLAFE-WALLAFE
  • TARO
  • bm sashe na 5 p. 8
  • Allah Ya Albarkaci Ibrahim da Iyalinsa

Babu bidiyo don wannan zabin

Yi hakuri, bidiyon na da dan matsala

  • Allah Ya Albarkaci Ibrahim da Iyalinsa
  • Littafi Mai Tsarki​—Wane Saƙo Ne Ke Cikinsa?
  • Makamantan Littattafai
  • Daga Tufana Zuwa Ceto Daga Ƙasar Masar
    Littafina na Labarun Littafi Mai Tsarki
  • Jehobah Ne “Allah Mai Ba Da Salama”
    Hasumiyar Tsaro Mai Shelar Mulkin Jehobah—2011
  • Taƙaici Daga Littafin Farawa—na II
    Hasumiyar Tsaro Mai Shelar Mulkin Jehobah—2004
  • Iyalin Ta Ƙaura Zuwa Ƙasar Masar
    Littafina na Labarun Littafi Mai Tsarki
Dubi Ƙari
Littafi Mai Tsarki​—Wane Saƙo Ne Ke Cikinsa?
bm sashe na 5 p. 8

Sashe 5

Allah Ya Albarkaci Ibrahim da Iyalinsa

Zuriyar Ibrahim sun sami albarka. Allah ya kāre Yusufu a ƙasar Masar

JEHOBAH ya san cewa Ƙaunataccensa zai sha wahala kuma zai mutu wata rana. Annabcin da ke rubuce a Farawa 3:15 ya ɗan ambata wannan gaskiyar a kaikaice. Allah zai iya nuna wa mutane yadda zai ji game da wannan mutuwar kuwa? Littafi Mai Tsarki ya kwatanta hakan. Allah ya gaya wa Ibrahim ya yi hadaya da ƙaunataccen ɗansa Ishaku.

Ibrahim yana da bangaskiya mai girma. Ka tuna, Allah ya yi masa alkawari cewa Mai Ceto, ko Zuriya, da aka annabta, zai fito daga Ishaku. Domin ya gaskata cewa Allah zai ta da Ishaku daga matattu idan da bukata, cikin biyayya Ibrahim ya tafi ya yi hadaya da ɗansa. Amma wani mala’ikan Allah ya hana Ibrahim yin hakan. Sa’ad da yake yaba wa Ibrahim domin ya amince ya yi hadaya da abu mafi tamani a wurinsa, Allah ya sake maimaita alkawuransa ga wannan uban iyali mai aminci.

Bayan haka, Ishaku ya haifi ’ya’ya biyu maza, Isuwa da Yakubu. Ba kamar Isuwa ba, Yakubu ya ɗauki abubuwa na ruhaniya da tamani kuma ya sami lada. Allah ya canja sunan Yakubu zuwa Isra’ila, kuma ’ya’yan Isra’ila su sha biyu sun zama shugabannin ƙabilun Isra’ila. Amma ta yaya wannan iyalin ta zama al’umma mai girma?

Hakan ya soma ne sa’ad da yawancin ’ya’yan Isra’ila suka soma kishin ƙaninsu Yusufu. Sun sayar da shi a matsayin bawa, kuma aka kai shi ƙasar Masar. Amma Allah ya albarkaci wannan matashi mai hikima da gaba gaɗi. Duk da wahalolin da ya sha, Fir’auna, sarkin Masar, ya zaɓi Yusufu, kuma ya ba shi iko mai girma. Hakan faɗuwa ce da ta zo daidai da zama, domin yunwa ta sa Yakubu ya aika wasu cikin ’ya’yansa zuwa ƙasar Masar don su sayo abinci, sai ya zamana cewa Yusufu ne ke kula da dukan abincin! Bayan sake haɗuwar da ya yi da ’yan’uwansa wanda hakan ke cike da motsin rai da mamaki, Yusufu ya gafarta musu kuma ya ce dukan iyalin ta komo ƙasar Masar. An ba su ƙasa mafi ni’ima, inda za su iya ci gaba da yaɗuwa kuma su sami albarka. Yusufu ya fahimci cewa Allah ne ya shirya al’amuran a wannan hanyar don Ya cika alkawuransa.

Yakubu wanda ya riga ya tsufa sosai, ya ci gaba da rayuwa ne a ƙasar Masar tare da iyalinsa da take ci gaba da girma, har mutuwarsa. Kafin ya mutu, ya annabta cewa Zuriya da aka yi alkawarinsa, ko kuwa Mai Ceto, zai kasance Sarki mai iko wanda zai fito ta hanyar ɗansa Yahuda. Kafin tasa mutuwar, Yusufu ya annabta cewa wata rana, Allah zai fitar da iyalin Yakubu daga ƙasar Masar.

—An ɗauko daga Farawa surori 20 zuwa 50; Ibraniyawa 11:17-22.

◼ Menene Allah ya gaya wa Ibrahim ya yi, kuma menene yake nuna wa ’yan Adam?

◼ Ta yaya Yusufu ya sami kansa a ƙasar Masar, kuma menene sakamakon?

◼ Menene Yakubu ya annabta kafin ya mutu?

[Taswira a shafi na 8]

● Farawa

Fitowa

Levitikus

Littafin Lissafi

Kubawar Shari’a

Joshua

Alƙalawa

Ruth

1 Sama’ila

2 Sama’ila

1 Sarakuna

2 Sarakuna

1 Labarbaru

2 Labarbaru

Ezra

Nehemiya

Esther

Ayuba

Zabura

Misalai

Mai-Wa’azi

Waƙar Waƙoƙi

Ishaya

Irmiya

Makoki

Ezekiel

Daniyel

Hosiya

Joel

Amos

Obadiya

Yunana

Mikah

Nahum

Habakkuk

Zafaniya

Haggai

Zakariya

Malakai

Matta

Markus

Luka

Yohanna

Ayyukan Manzanni

Romawa

1 Korintiyawa

2 Korintiyawa

Galatiyawa

Afisawa

Filibiyawa

Kolosiyawa

1 Tasalonikawa

2 Tasalonikawa

1 Timotawus

2 Timotawus

Titus

Filimon

Ibraniyawa

Yaƙub

1 Bitrus

2 Bitrus

1 Yohanna

2 Yohanna

3 Yohanna

Wasiƙa ta Yahuda

Ru’ya ta Yohanna

    Littattafan Hausa (1987-2026)
    Fita
    Shiga Ciki
    • Hausa
    • Raba
    • Wadda ka fi so
    • Copyright © 2026 Watch Tower Bible and Tract Society of Pennsylvania
    • Ka'idojin Amfani
    • Tsarin Tsare Sirri
    • Saitin Tsare Sirri
    • JW.ORG
    • Shiga Ciki
    Raba